in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Ministan harkokin waje na kasar Sin ya gana da babban sakataren AL
2017-09-22 20:40:59 cri
A jiya Alhamis ne, ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gana da babban sakataren kungiyar kasashen Larabawa(AL) Ahmad Abdoul Gheit a yayin da yake halartar babban taron MDD a birnin New York.

Mr.Wang Yi ya ce, Sin da kasashen Larabawa 'yan uwa ne, kana aminan juna ne. Sin na nuna yabo ga kasashen Larabawa bisa ga goyon bayan da suka ba ta kan batutuwan da suka shafi muradun kasar Sin da sauran muhimman al'amura, don haka, za ta ci gaba da kiyaye muradun kasashen Larabawa a batutuwan da ke jawo hankalinsu. Kasar Sin tana kuma son raba fasahohinta na samun ci gaban kasa tare da kasashen Larabawan.

A nasa bangare Mr.Gheit ya ce, kasashen Larabawa na dora muhimmanci sosai a kan bunkasa huldar da ke tsakaninsu da kasar Sin, kuma suna son hada kai da kasar Sin domin aiwatar da shawarar ziri daya da hanya daya.(Lubabatu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China