in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta amince da kudurin kwamitin sulhun MDD game da Koriya ta arewa
2017-12-23 13:08:28 cri
A yau Asabar, kwamitin sulhun MDD ya zartas da wani kuduri mai lamba 2397, kan harba makamai masu linzami da kasar Koriya ta arewa ta yi a watan da ya gabata, da nufin daukar matakan da suka dace na kara kakabawa kasar takunkumi.

Game da kudurin ne kuma, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin madam Hua Chunying ta ce kasarta na fatan ganin bangarori daban-daban sun yi biyayya yadda ya kamata, ga kudurorin kwamitin sulhun game da Koriya ta arewa, ciki har da kuduri mai lamba 2397, don warware matsalar zirin.

Madam Hua ta kara da cewa, kudurin mai lamba 2397, ya kara daukar matakan saka takunkuman da suka dace ga Koriya ta arewa, a waje guda kuma ya jaddada cewa, bai kamata ba matakan su haifar da mummunan tasiri ga fararen hula da harkokin tattalin arziki da hadin kai da taimakon jin kai ba. Kana kudurin ya sake nanata kiyaye zaman lafiyar zirin Koriya da yankin arewa maso gabashin Asiya, ya na mai kira da a warware matsalolin ta hanyar diplomasiyya cikin lumana.

Baya ga haka, madam Hua ta ce, har kullum, kasar Sin na tsayawa tsayin daka kan tabbatar da rashin kasancewar nukiliya a zirin, da kiyaye zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin, tare da dagewa wajen warware matsalar ta hanyar tattaunawa.

A cewarta, Wannan shi ne matsayin da a ko da yaushe, kasar ke dauka game da batun. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China