A yau Litinin ne hukumar ladaftarwa ta 18 JKS ta gudanar da zamanta na 8, inda aka tattauna tare da amincewa da rahoton aikin da aka gabatar mata don gabatarwa yayin babban taron wakilian JKS karo na 19 da ake sa ran budewa a ranar 18 ga wannan wata.
Bugu da kari, ana sa ran gabatar da rahoton a yayin zama na 17 na kwamitin tsakiya na JKS karo na 18 wanda za a bude a ranar 11 ga watan Oktoba, don tattaunawa a kai.
Mamban tsayayyen kwamitin hukumar siyasa na kwamitin tsakiya na JKS kana sakataren hukumar CCDI Wang Qishan shi ne ya yi wa kwamitin jawabi yayin ganawar.(Ibrahim)