in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Tawagar kafofin watsa labaru ta kasar Mozambique ta ziyarci lardin Heilongjiang na kasar Sin
2017-09-09 13:40:48 cri
Emilia Jubileu Moiane, darektar ofishin watsa labaru na kasar Mozambique, ta jagoranci wata tawagar da ta kunshi jami'an gwamnatin kasar masu kula da aikin watsa labaru, da shugabannin manyan kafofin watsa labarun kasar, wajen kai ziyara lardin Heilongjiang dake arewacin kasar Sin, daga ranar 6 zuwa 8 ga watan nan da muke ciki.

A yayin ziyarar, tawagar kafofin watsa labaru ta kasar Mozambique ta ziyarci wasu kamfanonin sarrafa amfanin gona, da cibiyar binciken fasahohin noma, da wurin adana kayayyakin tarihi na aikin gona, inda suka samu damar ganewa idanunsu yadda kasar Sin take kokarin zamanintar da fasahar aikin gona.

Haka zalika, mambobin tawagar sun ziyarci ofishin jaridar Heilongjiang Daily, inda suka tattauna kan matakan da za a bi don karfafa hadin gwiwar dake tsakanin bangarorin 2 a fannonin aikin watsa labarai da al'adu.

A cewar Madam Emilia Jubileu Moiane, kasar Mozambique tana da makeken fili, amma ba ta da fasahohin zamani na sarrafa amfanin gona, irin na lardin Heilongjiang na kasar Sin. Saboda haka, suna fatan ganin kasashen 2 za su kara yin hadin gwiwa a bangarorin da suka hada da shuka hatsi, da sarrafa amfanin gona, tare da habaka mu'amala a fannin al'adu, da zurfafa hadin gwiwa tsakanin hukumomin al'adu, da kafafen watsa labaru, na kasashen 2.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China