Kawo yanzu, ruwan sama ya rushe gidaje 1930 a kasar, baya ga makarantu 71 da asibitoci 5 da kuma madatsan ruwa 71 da suka lalace. Ruwan sama ya kuma rushe wasu hanyoyin mota da ma gadoji.
Rahotanni na nuni da cewa, goguwa mai lakabin Dineo da ta sauka a kudancin kasar Mozambique a ranar 15 ga watan Faburairun ita ma ta kawo illa ga kasar Zimbabuwe, wadda ta tagayyara mutane sama da dubu a sakamakon yadda ruwan saman da take tafe shi wanda ya lalata gidajensu.
Yanzu haka gwamnatin kasar ta Zimbabuwe da ma kungiyar Red Cross da sauran kungiyoyin duniya suna samar da abinci da ruwan sha da gidajen kwana na wucin gadi da jiyya ga al'ummar da bala'in ya shafa. (Lubabatu)