Kasar Sin ta kalubalanci kasashen Amurka ta Koriya ta kudu, game da shirinsu na girke na'urorin kandagarkin makamai masu linzami sanfurin THAAD a Koriya ta kudun.
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Geng Shuang wanda ya bayyana hakan a yau yayin taron manema labarai a birnin Beijing, ya ce kasar Sin tana kira ga kasashen biyu da su yi la'akari da harkokin tsaro da kuma muradun kasar Sin da ma na sauran kasashe, kana su gaggauta dakatar da shirin su na girke wadannan na'urori. (Ibrahim)