in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An sauke ragowar na'urorin THAAD a yankin Koriya ta kudu
2017-09-07 12:39:14 cri
Rahotanni daga Koriya ta kudu na cewa, da sanyin safiyar yau Alhamis ne Amurka ta girke sauran nau' oin na'urorin nan na kandagarkin makamai masu linzami sanfurin THAAD a wani yanki na koriya ta kudu.

Sakamakon wannan mataki, Amurka ta kammala shirin da ta yi, na sarrafa wadannan na'urori a duk lokacin da bukatar hakan ta taso. To sai dai kuma wannan lamari ya gamu da adawa daga dandazon masu zanga zanga a Koriya ta kudun.

An ce dakarun rundunar 'yan sandan kwantar da tarzoma, sun tare gungun masu zanga zanga su kusan 8,000, kana da tsakar daren jiya, 'yan sandan suka tarwatsa wasu masu jerin gwano, da masu rajin nuna adawa da shirin su kusan 400, wadanda ke kewayen unguwannin Seongju da na birnin Gimcheon dake kan iyakar kasar.

Tarzomar nuna adawa da kafa na'urorin THAAD, ta sabbaba jikkatar a kalla mutane 30, wadanda aka garzaya da su asibiti mafi kusa, kamar dai yadda kafofin watsa labarun yankin suka tabbatar.

Tun cikin watan Yulin shekarar da ta gabata ne dai al'ummun yankunan da aka girke wadannan na'urori, da masu kin jinin shirin girke su, ke ta kunna kyandira a ko wane dare, a biranen Seoul na Koriya ta kudu da Washington na Amurka, a wani mataki na adawa da manufa.

Da ma dai ma'aikatar tsaron Koriya ta kudun ta tabbatar da shirin da ake yi, na girke ragowar na'urorin a ranar Alhamis. Ma'aikatar ta ce hakan ya biyo bayan gwaje gwajen makamai masu linzami ne da Koriya ta arewa ke faman yi ne a baya bayan nan. (Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China