in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta bukaci Amurka da Koriya ta kudu da su dakatar da kafa na'urorin THAAD
2017-08-29 20:11:21 cri
Mai magana da yawun ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying, ta ce Sin na fatan Amurka da koriya ta kudu, za su dakatar da girke na'urorin kakkabo makamai masu linzami samfurin THAAD.

Hua Chunying ta ce Sin na fatan kasashen biyu, za su martaba manufofin tsaro da suka jibanci Sin da sauran kasashe dake yankin zirin koriya. Jami'ar ta yi wannan tsokaci ne yayin taron manema labarai da aka gudanar a yau, gabanin taron manyan jami'an tsaron kasashen na Amurka da koriya ta kudu a gobe Laraba.

Ta ce na'urorin THAAD ba za su magance kalubalen da kasashen wannan yanki na zirin koriya ke fuskanta ba. Maimakon haka matakin zai kara dagula yanayi ne kawai. Kaza lika hakan na iya gurgunta tsaron yankin baki daya ciki hadda Sin, tare da tsananta halin da ake ciki a zirin na Koriya.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China