Ta ce Sin da Kenya aminan juna ne, kuma 'yan uwa ne dake fatan ci gaba tare, a hannu guda kuma Sin na fatan fadada huldar diflomasiyyar ta da kasar Sin a dukkanin fannoni.
A ranar Juma'a ne dai hukumar zaben kasar Kenya ta IEBC, ta ayyana shugaban kasar Uhuru Kenyatta a matsayin wanda ya lashe zaben kasar na bana. A cewar shugaban hukumar ta IEBC Wafula Chebukati, shugaba Kenyatta ya samu kuri'u miliyan 8.20, adadin da ya kai kaso 54.27 bisa dari na jimillar kuri'un da aka kada. (Saminu Alhassan)