Shugaban kasar Xi Jinping, ya ce gwamnatin tsakiya ta kasar Sin za ta ci gaba da tallafawa yankin Hong Kong mai cin gashin kan sa, a fannin bunkasa ci gaban tattalin arziki da zamantakewar al'ummar sa.
Shugaba Xi ya bayyana hakan ne a Alhamis din nan, jim kadan bayan saukar sa a filin jirgin sama na kasa da kasa dake Hong Kong. Shugaban na Sin zai gudanar da ziyarar aiki ta kwanaki 3 a yankin, zai kuma halarci bikin cika shekaru 20 na komawar yankin Hong Kong din bangaren kasar Sin.
Kaza lika zai halarci bikin kaddamar da gwamnatin yankin ta biyar, da kuma gudanar da ziyarar aiki a wasu sassan yankin.(Saminu)