in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yi watsi da batun sakin dan tsohon shugaban Libya
2017-06-14 14:16:15 cri

Dakarun dake samun goyon bayan MDD a Libya, sun soki sakin dan tsohon shugaban kasar Saif Al-Islam Gaddafi. Dakarun sun ce, an shirya taron neman sulhunta sassan kasar karkashin hukumar dake da alhakin hakan a ranar Lahadi a Zintan, kuma a ra'ayin wakilan dakarun, sakin Saif Al-Islam Gaddafi ya sabawa doka, kuma cin amanar dubban wadanda suka rasa rayukan su ne, sakamakon kisan masu zanga zanga da shi Saif Al-Islam din ke da hannu a aikatawa.

Dakarun sun ce, za su yi bincike game da sakin Saif Al-Islam.

Rahotanni dai sun bayyana cewa, wasu dakaru da ke tsare da Saif Al-Islam Gaddafi ne suka sake shi a ranar Asabar din karshen mako, daga gidan yarin birnin Zintan, mai nisan kilomita 180 kudu maso gabashin birnin Tripoli.(Saminu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China