A ranar 7 ga watan da muke ciki ne dai wani jirgin saman jigila na rundunar soja mai dauke da fasinjoji 122 ya yi hadari, a kan hanyarsa daga birnin Mergui zuwa na Yangon. A kuma ranar 8 ga wata, rundunar sojan Myanmar ta sanar da fara aikin laluben tarkacen jirgin saman, da kuma gawawwakin fasinjojin dake cikinsa. (Fatima)