Shugaban kasar Sin Xi Jinping ya tashi daga nan birnin Beijing da yammacin yau Laraba zuwa kasar Kazakhstan, inda zai gudanar da ziyarar aiki, ya kuma halarci taron kungiyar hadin gwiwa ta Shanghai ko SCO a takaice.
Shugaba Xi zai kai ziyara Kazakhstan ne bisa gayyatar shugaban kasar Nursultan Nazarbayev. Daga bisani kuma ya halarci taron shugabannin kasashe mambobin kungiyar SCO karo na 17, da kuma bikin bude taron baje koli na duniya da za a gudanar a birnin Astana. (Saminu)