Jiya Laraba ne, a nan Beijing, sashen harkokin yin hadin gwiwa da ketare na ma'aikatar aikin gona ta kasar Sin da ofishin hukumar kula da abinci da aikin gona ta MDD wato FAO da ke nan kasar Sin suka kaddamar da shirye-shiryen da Sin da FAO za su gudanar daga shekarar 2016 zuwa 2020, inda suka tabbatar da fannoni 4 na yin hadin gwiwa a tsakaninsu, wato matakan bunkasar aikin gona mai dorewa da inganta kwarewar yaki da bala'i daga indallahi, rage kangin talauci da tabbatar da isasshen abinci da abubuwa masu gina jiki a yankunan karkara, kyautata lafiyar al'umma, da goyon bayan Sin wajen yin hadin gwiwa da shiyya-shiyya da ma duniya baki daya a fannin aikin gona. (Tasallah Yuan)