Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya furta a yau Alhamis cewa, kasar Sin na fatan kungiyar tarayyar Turai ta EU za ta gaggauta cika alkawarin da ta yi, cikin yarjejeniya mai alaka da shigowar kasar Sin cikin kungiyar cinikayya ta duniya WTO, ta yadda za a daina nuna bambanci ga kasar ta Sin bisa matsayinta a fannin cinikayya.
(Bello Wang)