in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Emmanuel Macron ya ci zaben sabon shugaban kasar Fransa
2017-05-08 10:59:39 cri
Bisa kididdigar da wasu hukumomin binciken ra'ayin jama'a na kasar Faransa suka bayar a daren jiya Lahadi, an nuna cewa, tsohon ministan tattalin arzikin kasar, kuma 'dan takarar jam'iyyar Movement "Forward" ta kasar Emmanuel Macron ya samu rinjaye bisa kuri'un da ya samu na sama da kashi 65 cikin dari da aka kada a zagaye na biyu na zaben shugaban kasar na shekarar 2017, ta hakan ya zama sabon zababben shugaban kasar Faransa. Macron 'dan shekaru 39 a duniya zai zama shugaba mafi karancin shekaru da aka taba samu a tarihin jamhuriyar kasar Faransa.

A yayin jawabin da ya yi ta gidan talibijin a daren ranar Lahadin, Macron ya ce, a cikin wa'adin aikinsa na shekaru biyar masu zuwa, zai yi iyakar kokarinsa wajen dinke barakar dake tsakanin al'ummar kasar.

Kafin jawabin nasa, abokiyar takararsa Marine Le Pen ta riga ta amince da shan kaye a zaben, ta kuma taya Macron murnar lashe zaben.

A nasa bangaren, shugaba Francois Hollande na kasar Farsansa, ya ba da sanarwa a daren wannan rana, inda ya ce ya riga ya taya Macron murnar lashe zaben.

Za a kawo karshen wa'adin aikin Hollande a ranar 14 ga wata. Bisa yadda aka saba, shugaba mai ci da shugaba mai barin gado za su tabbatar da lokacin bikin mika ragamar mulkin kasar.

Shugaban kasar Amurka Donald Trump, da shugaban kwamitin kungiyar EU Jean - Claude Juncker da dai sauransu sun taya Macron murnar lashe zaben shugaban kasa. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China