in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yan sanda a Masar sun kashe maharin yankin Sinai
2017-04-20 12:54:51 cri

Ministan harkokin cikin gidan Masar ya ce, 'yan sanda sun kashe wanda ya kai hari shingen binciken motoci a kudancin Sinai.

Cikin wata sanarwa da ya fitar a jiya, ministan ya ce, jami'an tsaro sun gano wurin da maharin ya buya, inda kuma suka kashe yayin musayar wuta.

Harin da aka kai ranar Talata kan wani shingen bincike dake kusa da mujami'ar St. Catherine a kudancin Sinai, ya yi sanadin mutuwar 'dan Sanda daya, tare da jikkata wasu guda hudu.

Wannan hari dai ya zo ne bayan kai wasu hare-hare kan mujami'u biyu a farkon makon da ya gabata, da suka yi sanadin rayukan mutane 47, harin da kungiyar IS ta dauki alhakinsa. (Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China