in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Gwamnatin Nijeriya za ta sake bude sakandaren Chibok na yanki arewa maso gabashin kasar mai fama da rikici
2017-04-14 10:14:02 cri
Gwamnatin Nijeriya ta ce, tana aiki tukuru don ganin an sake bude sakandaren gwamnati ta 'yan mata a Chibok, dake jihar Borno a yankin arewa maso gabashin kasar, domin fara daukar darasi a zango karatu na 2017/2018.

Mataimakin shugaban kwamitin shugaban kasar, kan farfado da yankin arewa maso gabas, Tijjani Tumsah, ya ce an dauki dukkan matakan da suka dace na tabbatar da ba a sake samun aukuwar makamancin abun da ya faru na sace 'yan mata a shekarar 2014 ba.

Tijjani Tumsah, ya ce za a samar da da wani tsari na samar da bayanai da yin gargadi kan lokaci domin tsaron 'yan matan.

Ya ce kwamitin na duba yuwar samar da wasu shirye-shirye da za su taimaka wajen saita tunanin matasan, ta yadda zai dace da manufofin gwamnati mai ci a kasar.( Fa'iza Mustapha)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China