in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin ta shirya taro game da samar da makomar bai daya ga bil Adama a karkashin UNHRC
2017-03-09 11:24:19 cri
A yanzu haka ake gudanar da taro karo 34 na majalisar kula da hakkin bil Adama ta MDD a birnin Geneva, inda tawagar kwamitin nazarin hakkin bil Adama ta kasar Sin, da zaunanniyar tawagar Sin dake MDD a Genewa suka shirya wani taro mai taken 'Samar da makomar bai daya ga dan Adam: Wadda sabuwar hanya ce ta gudanar da harkokin hakkin bil Adama a duk duniya'. Taron dai ya samu halartar kwararrun kasar Sin, da wakilan tawagar gwamnatocin kasashe sama da 20, da kuma wakilai na wasu kungiyoyi masu zaman kan su.

A yayin taron, kwararrun kasar Sin sun bayyana ra'ayin makomar bai daya ta bil Adama daga fannonin kalubalen da ake fuskanta a yanzu, da ra'ayoyin kare hakkin bil Adama, da yadda ake kiyaye hakkin bil Adama bisa tsarin makomar bai daya ta dan Adam, da rawar da Sin ke takawa wajen gudanar da harkokin hakkin bil Adama na duniya, da manufofin da Sin ke bi a fannin addinai da ayyukan da ta zartar wajen samar da makomar bil Adama ta bai daya.

Kana wakilan da suka fito daga kasashen Rasha, da Pakistan da Cuba da dai sauransu, sun gabatar da tambayoyinsu a fannonin rawar da kungiyoyin kula da hakkin bil Adam masu zaman kan su a kasar Sin suke takawa, wajen gudanar da harkokin bil Adama na duniya, sun kuma tattauna matuka tare da kwararrun kasar ta Sin. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China