in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta rage haraji ga iyalan dake da 'ya'ya biyu
2017-03-07 19:51:04 cri
Mahukunyan kasar Sin suna shirin bullo da wani shiri da zai kai ga rage biyan haraji ga iyalan da suka haifi 'ya'ya biyu.

Ministan kudi na kasar Sin Xiao Jie wanda ya bayyana hakan yayin taron manema labarai a gefen taron shekara-shekara na manyan tarukan kasar biyu wato taron majalisar wakilan jama'ar kasar Sin, da taron majalisar ba da shawara kan harkokin siyasar kasar da ke gudana yanzu haka a nan birnin Beijing, ya ce kasar Sin tana shirin yiwa tsarin biyan haraji gyaran fuska, ta yadda za a rika biyan haraji kan wasu kudaden albashin ma'aikata.

Ministan Xiao ya ce kudaden da iyalai masu 'ya'ya biyun ke kashewa ga misali kudin makaranta suna daga cikin wadanda za a rage harajin da ake biya a kai.

A karshen shekarar 2015 ne masu tsara dokokin na kasar Sin suka yiwa dokar tsarin iyali gyaran fuska, matakin da ya baiwa dukkan iyalai zabin haifar 'ya'ya biyu. (Ibrahim Yaya)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China