in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta aiwatar da matakan rage hauhawar alkaluman bashin ta in ji wani kusa a babban bankin kasar
2017-02-24 12:39:16 cri
Kwararren a fannin tattalin arziki, kuma kusa a babban bankin kasar Sin Ma Jun, ya ce a bana kasar sa za ta aiwatar da wasu tsare tsare, wadanda za su kyautata hada hadar kudade, ta yadda za a kai ga kaucewa fadadar bashin da ake bin ta, tare da tashin gwauron zabi na farashin wasu kadarori.

Ma Jun ya bayyana hakan ne a jiya Alhamis, yayin wani taron masu ruwa da tsaki game da tattalin arziki da aka gudanar a Singapore. Ya ce manufofin da ake shirin aiwatarwa za su taimaka, wajen daidaita matsayin tattalin arzikin kasar, a gabar da Sin din ke daukar matakai na kara bude kasuwar cinikayyar takardun basukan ta, tare da samar da damammaki na shigar da su cikin gamayyar kasuwannin hannayen jari na kasa da kasa.

Mr. Ma ya kara da cewa, hukumar dake lura da hada hadar musayar kudaden waje, na daukar matakan samar da ka'idoji, wadanda za su bada dama ga masu zuba jari karkashin inuwar bankunan kasashen waje, ta yadda za su shiga kasuwannin musayar kudi na cikin gidan kasar.

Kaza lika ana duba yiwuwar fadada lokutan hada hadar takardun basussuka tsakanin bankuna daban daban, tare da inganta hadin gwiwa tsakanin cibiyoyin cinikayyar takardun bashin kasar.(Saminu Alhassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China