in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin za ta kirkiro sabbin ayyuka miliyan 50 nan da 2020
2017-02-07 10:29:13 cri

Majalisar gudanarwar kasar Sin ta sanar a jiya Litinin cewa, za ta samar da guraben ayyukan yi kimanin miliyan 50 a garuruwan kasar nan da shekarar 2020.

Majalisar gudanarwar ta bayyana shirinta na samar da ayyukan yi na shekarun 2016-2020, da cewa muhimmnin batu ne na inganta rayuwar al'umma da kuma habaka ci gaban tattalin arziki.

Kasar Sin ta dukufa matuka wajen samar da ayyukan yi masu yawan gaske, musamman wajen harkokin da suka shafi kasuwanci domin fadada hanyoyin ci gaban tattalin arziki.

Gwamnatin kasar Sin za ta tallafawa dalibai da suka kammala karatunsu, da manoma da ma'aikata, don ba su ayyukan yi, don rage cinkoso a ma'aikatu da kamfanani masu zaman kansu.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China