in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Algeria ta ce MDD na aiwatar da ayyukan wanzar da zaman lafiya guda tara a Afrika
2016-12-19 09:35:18 cri

Ministan harkokin wajen kasar Algeria Ramtane Lamamra ya ce, majalisar dinkin duniya na aiwatar da shirye-shiryen wanzar da zaman lafiya guda tara a nahiyar Afrika.

Da yake ganawa da manema labarai a wani bangare na wani taron bita kan tsaro a Algeria, ministan ya ce, daga cikin ayyukan wanzar da zaman lafiya goma sha shida da majalisar ke aiwatarwa a fadin duniya, guda tara sun kasance a nahiyar Afrika

Ya ce, dole ne majalisar ta kara karfafa hadin kai da hukumomin tarayyar Afrika a wannan tsari, domin samun ingantaccen zaman lafiya mai dorewa.

Baya ga shirin MINURSO mai shirya yarjejeniyar zaman lafiya a yankin yammacin Sahara dake fama da rikice-rikice, sauran wurare takwas da ake aiwatar da shirye-shiryen sun hada da Liberia, da Cote d'Ivoire, da Jamhuriyar Demokradiyyar Congo, da Sudan, da Sudan ta Kudu, da Darfur, da Mali, da kuma Afrika ta Tsakiya. (Fa'iza)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China