Xi Jinping ya aika sakon jaje ga shugaban kasar Masar
A jiya Talata ne, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya aika wa takwaransa na kasar Masar Abdel Fattah al Sisi sakon nuna jaje, inda ya janjanwa shugaba Fattah Al Sisi da iyalan wadanda suka rasa rayukansu a harin bam din da aka kai kan wani coci a ranar11 ga watan. Mr. Xi ya jaddada cewa, kasar Si ta yi tir da kakkausar murya kan wannan harin na ta'addanci, ta kuma tsaya tsayin daka kan matsayin dakile duk wani nau'i na ta'addanci. Haka kuma shugaba. Xi ya ce, kasar Sin za ta ci gaba da nuna goyon baya ga kasar Masar a kokarin da take yi na tabbatar da zaman lafiya da dakile ayyukan ta'addanci. (Sanusi Chen)
Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku