A yau ne yarjejeniyar sauyin yanayi da aka cimma a birnin Paris na kasar Faransa ta fara aiki a hukumance.
Game da lamarin, madam Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana cewa, a matsayinta na kasa mai tasowa wadda ke sauke nauyinta yadda ya kamata, kasar Sin ta ba da kyakkyawar gudummawa wajen cimma yarjejeniyar Paris da ta fara aiki da ita. Fara aiki da yarjejeniyar ta Paris, wani sabon mafari ne a fannin daidaita sauyin yanayi a duk fadin duniya, kuma zai jagoranci kasashen duniya shiga sabon mataki na samun ci gaba ba tare da gurbata muhalli ba. (Tasallah Yuan)