in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin za ta kara ba da gudummowa wajen kiyaye hakkin dan Adam na duniya
2016-10-31 19:48:48 cri

Madam Hua Chunying, kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin ta bayyana yau Litinin a nan Beijing cewa, kasar Sin za ta yi amfani da damar zama mamban kwamitin kula da kare hakkin dan Adam wajen kara ba da babbar gudummowa a fannin kiyaye hakkin dan Adam a duniya.

A ranar 28 ga wata ne babban taron MDD karo na 71 ya jefa kuri'ar zaben mambobin kwamitin harkokin kare hakkin dan Adam na shekarar 2017 zuwa shekarar 2019, inda kasar Sin ta samu kuri'u 180, wanda ya ba ta damar zama mamban kwamitin a karo na 4 tun bayan kafuwar kwamitin. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China