in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mataimakin shugaban Najeriya ya bukaci kamfanonin Sin da su tallafawa kasarsa a fannin fasahar zamani
2016-10-26 10:07:24 cri

Kwanan baya ne, mataimakin shugaban kasar Najeriya Yemi Osinbajo ya gana da shugabannin kamfanonin kasar Sin 2 da wasu jami'an ofisoshin jakadancin kasar Sin da ke kasar a fadar shugaban kasar da ke Abuja.

A yayin ganawar, Osinbajo ya yi maraba da shugabannin kamfanonin kasar Sin 2 da hannu bibbiyu. Yana mai da cewa, gwamnatin Najeriya tana ba da muhimmanci game da raya hulda a tsakaninta da kamfanonin kasar Sin, sakamakon yadda hadin gwiwar da ke tsakanin sassan 2 za ta taimakawa gwamnatin Najeriya matuka. Ya kuma jaddada cewa, gwamnatinsa tana kara azama wajen kera kayayyaki a kasar, don haka tana son inganta hadin kai da kamfanonin kasar Sin, musamman ma a fannin fasahar zamani, a kokarin raya aikin kera kayayyaki a kasar ta Najeriya.

Shugabannin wadannan kamfanonin Sin guda 2 sun ziyarci kasar Najeriya ne bisa gayyatar mista Chukuma Innocent Ifediaso, shugaban kamfanin Innoson, kana shugaban masu masana'antu da 'yan kasuwa na Najeriya.

Sun fara ziyarar tasu ce a ranar 24 ga wata, inda suka yi rangadi a fannin kulla hadin gwiwa tsakanin kafofin yada labaru, dangane da yadda za su kulla yarjejeniya a fannin watsa shirye-shiryen telibijin na zamani. (Tasallah Yuan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China