Wata kafar talabijin mai suna Canal3 ta ba da rahoton cewa, fashewar ta samo asali ne daga rububbiyar filawa da ba ta gama konewa a filin da ake kona irin wadannan shara ba kimanin kilomita 20 arewa da birnin Cotonou.
Rahotanni na bayyana cewa, mutane da dama sun jikkata a lokacin da jama'a ke ribibin kwasar filawar da ta rube, bayan da jami'an da ke sanya ido sun bar wurin da ake kona sharar.(Ibrahim)