Jiya Alhamis dakarun tabbatar da zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afrika (AU) dake samun goyon bayan rundunar sojojin kasar Somaliya (ANS) sun karbi wani muhimmin yanki dake kudancin Somaliya daga hannun mayakan kungiyar Al-Shabaab.
Dakarunmu na AU da na ANS sun karbi ikon mamaye yankin Abdalla Birole. Mayakan Al-Shabaab sun tsere daga yankin, kuma ba a samu mutuwa ko jikkata daga wajen mutanenmu a yayin wannan samame, in ji Joe Kibet, kakakin dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar AU dake Somaliya (AMISOM).
Yankin Abdalla Birole na kusan kilomita 60 daga yammacin kauyen Kismayo, hedkwatar mulki ta jihar Jubaland dake kudancin Somliya. (Maman Ada)