in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Bongo ya ki amincewa a sake kidiya kuri'un da aka kada
2016-09-07 20:06:41 cri
Shugaban kasar Gabon da aka sake zaba Ali Bongo, ya yi watsi da kiraye-kirayen da ake na sake kidaya kuri'un da ake takaddama a kansu.

Bongo ya shaidawa radiyon kasar Faransa na RTL cewa, ba zai karya doka ba. A cewarsa kotun tsarin mulki kasa ce kadai ke da ikon ba da umarnin sake kidiya kuri'un da aka kada.

A makon da ya gabata ne dai rikici ya barke a kasar da ke tsakiyar Afirka, bayan da 'yan adawa suka nuna rashin amincewa da sakamakon zaben da ya baiwa shugaba Bongo nasarar sabon wa'adin mulki na tsawon shekaru 7.

Rahotanni na cewa, tashin hankalin da ya barke a kasar yayi sanadiyar mutuwar mutane 3 kana wasu daruruwa suka jikkata.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China