in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kasar Sin: An tabbatar da burin da ake fatan cimmawa a taron G20
2016-09-06 18:47:36 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Hua Chunying ta yaba sosai kan sakamakon da aka samu a taron kolin G20 da aka shirya a Hangzhou da ke nan kasar Sin.

Madam Hua ta bayyana haka ne a yau Talata a yayin taron manema labaru da aka saba shiryawa, ta ce, an shirya taron kolin a daidai lokacin da ake neman hanyoyin raya tattalin arzikin duniya, da canja tsarin G20, saboda haka taron ya jawo hankulan al'ummomin kasashen duniya sosai.

A yayin taron, kasar Sin ta sanya bangarori daban daban da suka halarci taron wajen tattauna manufofin samun ci gaban tattalin arzikin duniya da hadin kai a tsakaninsu, kana an cimma muhimmin ra'ayi bai daya kan wasu batutuwa. (Bilkisu)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China