in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
UNICEF: kashi 40 cikin 100 na yara a kasashe 10 ba sa makaranta
2016-09-02 09:49:40 cri
Asusu tallafawa kananan yara na MDD(UNICEF) ya bayyana cewa, kimanin yara miliyan 18 ne ba sa zuwa makaranta, a wasu kasashe 10 mafi fama da matsala a fannin ilmantar da yara.

Wani rahoton da asusun na UNICEF ya fitar, ya nuna cewa, kasar Liberia ce ta ke kan gaba a wannan matsala,inda kimanin kaso biyu bisa uku na yaran da suka cancanci shiga makarantar firamare a kasar ba sa samun damar zuwa makarantar. Kasar Sudan ta Kudu ce ta biyu da kaso 59 na yaran da ba sa zuwa makarantar firamare, sai kasar Afghanista mai kaso 46 cikin 100,Nijar na da kaso 38, sai kuma Najeriya mai kaso 34 cikin 100 na yaran da ba sa samun damar zuwa makarantar firamare. Sai dai kuma rahaton asusun na Unicef bai ambaci kasashen Somaliya da Syria ba, saboda yake-yaken da ke faruwa a kasashen.

Bayanan na Unicef sun dora alhakin matsalar da ke faruwa a wadannan kasashe ne kan tashe-tashen hankula,matsalar fari,ambaliyar ruwa, girgizar kasa da kangin talauci.

Sai dai kuma, asusun ya ce, yana fargabar cewa,yaran da ke zaune a wadannan kasashe, za su girma ba tare da wata sana'a ko kwarewar da suke bukata don taimakawa ci gaban tattalin arikin kasashensu ba.

Rahotanni na nuna cewa, duk da kiraye-kirayen da ake yi na neman bunkasa bangaren ilimi,har yanzu kaso 31 cikin 100 kawai aka samu.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China