Sakatare janar na MDD ya yi marhaba da amincewar Sudan ta Kudu da tura sojojin kasa da kasa domin kare al'ummar kasar daga tashe-tashen hankalin tsakanin bangarorin kasar masu gaba da juna. Sudan ta Kudu ta tsai da wannan kuduri ne a lokacin zaman taro na kasa da kasa wanda ya hada da kasashen da ke gabashin nahiyar Afirka. Mista Ban ki-Moon ya yi kira ga bangarorin kasar masu gaba da juna wajen kawo karshen tashe-tashen hankalin cikin kasar domin aiwatar da yarjejeniyar shimfida zaman lafiya a kasar. (Laouali Souleymane)