in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An soke Zambiya a wasannin kwallon kafa na kudancin Afrika saboda magudin shekaru
2016-08-02 16:31:21 cri
An fitar da kasar Zambiya daga gasar wasannin kwallon kafa na 'yan kasa da shekaru 17, wanda hukumar wasan kwallon kafa ta kasashen kudancin Afirka ko (COSAFA) ke shiryawa, sakamakon yin magudin shekaru.

Jami'an shirya gasar sun tabbatar da hakan a Juma'ar data gabata, inda suka ce an fitar da kungiyar 'yan wasan kwallon kafan kasar Zambiyan ne, bayan wani gwaji da aka gudanar, inda sakamakon gwajin ya nuna cewar biyu daga cikin 'yan wasan kasar shekarunsu sun zarta 17.

Kasar Zambiya ta mika 'yan wasan gabanta biyu wato Nicholas Mulilo da Benjamin Phiri bisa radin kanta, domin sake yi musu gwaji a wasannin wanda ake gudanarwa a Mauritius, bayan korafe korafen da wasu kasashe biyu suka yi game da 'yan wasan.

Sanarwar ta bayyana cewa, an yi waje da kasar Zambiya ne, bayan sake gwajin da aka gudanar a kan Nicholas Mulilo, da Benjamin Phiri a Mauritius, bayan an gano sun dara shekaru 17 da haihuwa, wanda ya saba da sashe na 10.5 (1) na dokokin wasannin kwallon kafar hukumar.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China