in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Aljeriya da Nijer za su kulla dangantaka don samar da tsaro
2016-07-27 10:00:58 cri

A ranar Talata kasashen Aljeriya da Nijer suka tattauna hanyoyin da za su kulla dangantakar yaki da ta'addanci da tabbatar da tsaro a yankunan kudu da hamadar Sahara.

Ministan harkokin wajen Nijer Ibrahim Yakubu ya fadawa 'yan jaridu cewar, bayan tattaunawa da takwaransa na Aljeriya Ramtane Lamamra, kasashen Nijer da Aljeriya sun amince za su karfafa hadin gwiwa a tsakaninsu domin tabbatar da tsaro a yankunan.

Babban jami'in diplomasiyyar na jamhuriyar Nijer ya tabbatar da cewar, akwai kyakkyawar mu'amala da fahimtar juna tsakanin kasashen biyu dake makwabtaka da juna, sannan ya yabawa kasar Aljeriya bisa irin kokarin da take wajen yaki da ta'addanci.

Kasar Ajriya ta girke dakaru a kudancin kasar mai tazarar kilomita 1,200 dake makwabtaka da kasashen Mali da Nijer, domin dakile aniyar bazuwar makamai da 'yan tawaye a yankunan.(Ahmad Fagam)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China