in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mauritania ta samar da lambobin yabo ga likitocin kasar Sin
2016-07-24 11:57:02 cri
Gwamnatin kasar Mauritania ta shirya wani bikin samar da lambobin yabo ga likitocin kasar Sin masu ba da tallafi ga aikin jinya a kasar, a Nouakchott, fadar mulkin kasar, a ranar Jumma'ar da ta wuce.

Wadannan likitoci Sinawa suna cikin tawagar masu aikin likitanci da kasar Sin ta tura ma kasar Mauritania a karo na 31, wadanda suka kammala wa'adin aikinsu da kuma za su dawo kasar Sin. Dalilin haka ne, aka shirya bikin domin yaba musu kan kokarin da suka yi na raya aikin likitanci a kasar Mauritania, da kara dankon zumuncin dake tsakanin kasashen 2.

Wasu manyan jami'an da suka hada da Boubacar Kan, ministan kiwon lafiya na kasar Mauritania, da Wu Dong, jakadan kasar Sin dake Mauritania, sun halarci bikin ba da lambobin yabo din, inda minista Boubacar Kan, a madadin shugaban kasarsa Mohamed Ould Abdel Aziz, ya mika takardun shaidar yabo ga likitocin kasar Sin, tare da nuna musu godiya kan gudunmowar da suka bayar a fannonin raya aikin jinya a kasar, da tabbatar da lafiyar jikin jama'ar kasar.(Bello Wang)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China