in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Hukumar tsaron Somaliya ta kama mayakan Al-Shabaab
2016-06-01 10:24:43 cri
Rahotanni daga kasar Somaliya na cewa, hukumar leken asiri da tsaron kasar ta yi nasarar damke mayakan Al-Shabaab guda 4 yayin suke kokarin kaddamar da wasu hare-haren a wajen birnin Mogadishu, babban birnin kasar.

Kakakin ma'aikatar tsaron cikin gidan kasar Abdikamil Moalin Shukri ya bayyana cewa, dakarun tsaron kasar sun yi nasarar kwace wata mota makare da abubuwan fashewa, a lokacin da suka kaddamar da wani samamen da ya kai ga kama mayakan kungiyar guda 4 a yankin Elasha-biyaha da ke kudancin birnin Mogadishu.

Rahotanni na nuna cewa, a 'yan watannin da suka gabata sojojin Somaliya da ke samun goyon bayan dakarun wanzar da zaman lafiya na kungiyar tarayyar Afirka, sun samu nasara a yakin da suke yi da mayakan na Al-Shabaab. Koda ya ke har yanzu kungiyar tana kai hare-hare a sassan kasar daga lokaci zuwa lokaci.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China