in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'ai daga Sin da Amurka za su gudanar da dandalin tattaunawa na shekara-shekara
2016-05-30 20:37:39 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya bayyana cewa wakilai daga tsagin kasar Sin da takwarorin su na Amurka, za su gudanar da dandalin tattaunawa na shekara shekara, game da batutuwan da suka jibanci tattalin arziki da kuma musaya tsakanin sassan biyu.

Za dai a gudanar da taron (S&ED) na tattalin arziki, da na (CPE) wanda ya shafi musaya tsakanin al'ummun kasashen biyu ne a nan birnin Beijing, a ranekun 6 da 7 ga watan Yuni mai zuwa.

Ana dai sa ran mataimakin firaministan kasar Sin Wang Yang, da dan majalissar zartaswar Sin Yang Jiechi ne za su jagoranci taron da ya jibanci tattalin arziki, yayin da kuma mataimakiyar firaministan kasar Sin Liu Yandong da sakataren wajen Amurka John Kerry za su jagoranci taron musaya tsakanin kasashen biyu. Harkar musaya tsakanin sassan biyu dai ta kunshi fannin ilimi, da na kimiyya da fasaha, da raya al'adu, da kiwon lafiya. Sauran sun hada da inganta harkar wasanni, da bunkasa rayuwar mata da matasa.

Da yake tsokaci game da gudanar da tarukan, Mr. Lu ya bayyana cewa Sin na da nufin aiwatar da manufofin da ke karkashin yarjeniyoyin da ta cimma da Amurka, don haka ya dace sassan biyu su ci gaba da bunkasa hadin gwiwa tare da warware banbance banbancen dake tsakaninsu. Kana su kara azama wajen gina sabon tushen ma'amala tsakanin su. (Saminu Hassan)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China