in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Kakakin ma'aikatar harkokin tsaron kasar Sin ya yi jawabi game da jirgin ruwan yaki na Amurka da ya shiga Nanhai
2016-05-11 13:31:20 cri
Rahotannin daga shafin yanar gizo na ma'aikatar harkokin tsaron kasar Sin na cewa kakakin ma'aikatar Yang Yujun, ya yi jawabi game da jirgin ruwan yaki na Amurka ya yi kutse a yankin tekun tsibirai dake tekun kudancin kasar Sin na Nanhai.

Yang Yujun ya bayyana hakan ne jiya Laraba, yana mai cewa jirgin ruwan yaki samfurin Lawrence ya yi kutse a yankin takun tsibiran na Nanhai na kasar Sin ba tare da samun izini daga kasar Sin ba. Kana sojojin kasar Sin sun dauki mataki kan hakan ba tare da bata lokaci ba.

Yang Yujun ya bayyana cewa, shigar jirgin ruwan yakin na Amurka yankin tekun Nanhai na kasar Sin, ba zai canja matsayin mallakar wannan yanki na kasar Sin ba. Ya ce tsokanar da Amurka ta yi ba ta da wani tasiri. Har ila yau a cewar Mr. Yang, Sin za ta ci gaba da aikin sintiri a yankin tekun, da sararin sama bisa bukatu. Za kuma ta kara inganta karfin kiyaye tsaro, da tabbatar da ikon mallakar yankunan ta, tare da kuma kiyaye zaman lafiya da tsaro a yankin tekun Nanhai na kasar. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China