in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Sin ta yabawa ministan harkokin wajen Rasha kan zancensa game da batun tekun Nanhai
2016-04-13 21:18:57 cri
Kakakin ma'aikatar harkokin wajen kasar Sin Lu Kang, ya yabawa ministan harkokin wajen Rasha Sergei Lavrov game da ra'ayin da ya bayyana kan batun tekun Nanhai.

Kafin haka Sergei Lavrov, ya bayyana ma 'yan jarida na kasashen Sin da Japan da Mongolia cewa, ya kamata dukkan kasashen da batun tekun Nanhai ya shafa, su bi hanyar diplomasiyya don warware batun. Sannan yayi gargadin cewa, ya zama wajibi ga kasashen da ba su da nasaba da batun kai tsaye, su dakatar da duk wane yunkurin tsoma baki kan wannan batu, ko kuma mayar da batun a matsayin batun siyasar duniya. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China