in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rundunar sojan Amurka ta musunta aikata laifin yaki game da harin bom kan wani asibitin Afghanistan
2016-04-30 13:48:22 cri
A jiya Jumma'a, ma'aikatar tsaron Amurka ta gabatar da sakamakon bincike dangane da kai harin boma kan asibitin (Medecins sans Frontieres) MSF a kasar Afghanistan a shekarar 2015, inda ta bayyana cewa kaddamar da harin ba da gangan ba ne, wannan dalilin ne ya sa ba zai kasance aikata laifin yaki ba.

Dangane da wannan batu, kungiyar kula da lafiya ta MSF ta mai da martani cewa, sakamakon binciken da hukumar Pentagon ta Amurka ta fitar ya nuna cewa, rundunar sojan Amurka ba ta ba kyakkyawar kulawa ga aikin soja da ta dauka a yankin dake cike da fararen hula ba, kuma ba ta bi ainihin ka'idar yake-yake ba.

Shugabar kungiyar MSF, madam Meinie Nicolai ta ba da sanarwar cewa, ko a Afghanistan, ko a Syria, ko kuma a Yemen, bai kamata kungiyoyin dakaru su gudu daga daukar alhakinsu bisa dalili na wai ba da gangan ba su kaddamar da hare-hare kan asibiti ba.

Madam Nicolai ta sake yin kira da a kafa wani kwamiti na kasa da kasa mai zaman kansa domin yin bincike kan wannan batu.

A ranar 3 ga watan Oktoban bara ne, sojojin Amurka suka kai hari ta jiragen sama kan wata cibiyar jiyya ta kungiyar MSF dake garin Kunduz a arewacin Afghanistan, wanda ya haddasa mutuwar fararen hula 42, ciki har da jami'an kungiyar MSF su 14.

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China