in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Rukunin 'yan sandan kiyaye zaman lafiya na hudu da Sin ta tura zuwa Liberiya ya sauya wurin aiki
2016-03-28 10:11:19 cri
A ranar Asabar 26 ga wata, rukunin 'yan sandan kiyaye zaman lafiya na 4 da Sin ta tura zuwa Liberiya domin daukar nauyin tabbatar da tsaron ma'aikatar harkokin waje ta kasar a hukunce. Wannan ne karo na farko da ta gudanar da aiki bayan canja wurin aikinta zuwa birnin Monrovia, hedkwatar kasar Liberiya.

A safiyar wannan rana da misalin karfe 7, rukunin 'yan sandan kiyaye zaman lafiya na 4 na Sin ya karbi aiki daga hannun rukunin 'yan sandan Jordan a babbar kofar ma'aikatar harkokin waje ta Liberiya.

Tun shekarar 2015 zuwa yanzu, tawagar musamman kan batun Liberiya ta MDD ta rage rundunonin sojojin kiyaye zaman lafiya na kasashe da dama a Liberiya. Rukunin 'yan sanda ta 4 ta Sin ta sauya wuri daga birnin Greenville dake kudu maso gabashin kasar zuwa birnin Monrovia, hedkwatar kasar. A sabili da haka, ta zama rundunar daya tak dake tabbatar da zaman lafiya a hedkwatar kasar, wadda ke daukar nauyin ba da kariya ga babban ginin ma'aikatar harkokin waje. Idan an kai hari ko yin barazana a kai, dole ne kungiyar ta ba da agaji ga hukumomi masu tabbatar da tsaro cikin lokaci.(Fatima)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China