in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Najeriya: 'Yan sanda sun cafke wasu komandojin Boko Haram da ake nema ruwa jallo
2016-03-25 09:48:11 cri
'Yan sandan Najeriya sun tabbatar a ranar Alhamis da cafke wasu komandojin kungiyar Boko Haram da ake nema ruwa jallo a jihar Taraba, da ke arewa maso gabashin kasar Najeriya.

An mika Ali Audu da Abdulmumini Abdullahi a hannun rundunar sojojin Najeriya da ke jihar Yobe mai makwabtaka, in ji Shaba Alkali, shugaban 'yan sandan jihar Taraba, kafin ya kara da cewa an cafke kowanansu a ranar 22 ga watan Fabrairu da ranar 5 ga watan Maris.

Mutanen biyu suna cikin takardar jerin sunayen mambobin Boko Haram da ake nema ruwa jallo da rundunar sojojin Najeriya ta fitar a shekarar da ta gabata.

A kalla kamandojin Boko Haram kusan biyar ne rundunar ta cafke a shekarar da ta gabata a wasu yankunan kasar.

Boko Haram ta kashe dubun dubatar jama'a a Najeriya tun farko kaddamar da ayyukanta a shekarar 2009 bisa yunkurinta na kafa kasar musulunci.

Gwamnatin Najeriya ta bayyana cewa ta karya lagon wannan kungiya, amma har yanzu mayakanta na cigaba da kai hare hare jehi jehi a wannan kasa da ke yammacin Afrika. (Maman Ada)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China