in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An yabawa Sin bisa kokarinta na kare namun daji da tsirrai a nahiyar Afirka
2016-03-04 11:03:53 cri
A jiya Alhamis 3 ga wata wato ranar kare namun daji da tsirrai ta duniya, mataimakin babban sakataren MDD kuma direktan hukumar shirin kiyaye muhalli na MDD wato UNEP Achim Steiner ya bayyanawa 'yan jaridan kamfanin dillancin labaru na Xinhua cewa, gwamnatin kasar Sin da kamfanoni da jama'ar kasar sun ba da gudummawa wajen kare namun daji da tsirrai a nahiyar Afirka. MDD, Sin da kuma kasashen Afirka suna da damar hadin gwiwa a fannin kiyaye muhalli.

Achim Steiner ya bayyana cewa, a cikin shekaru biyu zuwa uku da suka gabata, gwamnatin kasar Sin ta sha gabatar da dokokin kiyaye muhalli da dama, da tsara matakai don kare namun daji da tsirrai a nahiyar Afirka, don haka shugabannin kasashen Afirka suka yaba wa kasar Sin. Kana ya kara da cewa, gwamnatin kasar Sin ta dora muhimmanci sosai ga kiyaye muhalli da samun bunkasuwa ba tare da gurbata yanayi ba, kuma wannan shi ne burin Sin da shirin kiyaye muhalli na MDD wato UNEP. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China