in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An rufe taron koli na kungiyar EAC
2016-03-03 11:13:41 cri
A ranar Larabar data gabata, an rufe taron koli na kungiyar kawancen kasashen gabashin Afrika EAC a birnin Arusha dake arewacin kasar Tanzaniya.

Shugabannin kasashen Tanzaniya, Kenya, Uganda da Ruwanda na daga cikin wadanda suka halarci taron.

Shugaban kasar Tanzaniya John Magufuli mai rike da shugabancin karba-karba na kungiyar ya sanar a taron cewar, kungiyar za ta shigar da kasar Sudan ta kudu don zama mambarta ta shida. Sudan ta kudu ta gabatar da bukatarta ta shiga kunigyar ne, bayan da ta samu 'yancin kanta a shekarar 2011, daga bisani kungiyar ta kafa wani kwamitin ministoci don yi mata bincike.

Ban da wannan kuma, saboda ganin mawuyancin hali da kasar Burundi ke ciki a halin yanzu, taron ya yanke shawarar dage wa'adin shugabancin kasar Tanzaniya zuwa shekarar 2017. Dadin dadawa, shugabanni masu halartar taron sun sanar da gabatar da sabuwar takardar iznin shiga gabashin Afrika ta yanar gizo don ingiza dunkulewar gabashin Afrika gaba daya. (Amina)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China