in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Mutane kusan 18 ne suka mutu a wani harin kunar bakin wake a arewa maso gabashin Nigeriya
2016-01-30 12:01:36 cri
Rahotanni daga Nigeriya sun tabbatar da cewar a kalla mutane 18 ne suka mutu wadansu da dama kuma suka jikkata sakamakon wani harin kunar bakin wake da aka kai a ranar kasuwa a garin Gombi na jihar Adamawa ranar jumm'an nan.

Harin da aka kaddamar dai wani yaro ne matashi ya aiwatar da shi bayan da ya saka bam din a cikin singiletin dake jikin shi a babbar kasauwar ta garin Gombi wanda hakan yasa yawancin wadanda harin ya rutsa dasu masu wucewa dake kusa da shi, inji wani da ya shaida da idanun shi Malam Ismail Gambo.

Mazauna garin dai sun dora alhakin wannan harin akan kungiyar boko haram masu tsatsauran ra'ayi da ikirarin zasu kafa daular musulunci a kundin tsarin mulkin kasar.

A baya ma dai, garin Gombi ya taba fuskantar harin wannan kungiyar bayan da suke ta kokarin kwace garin bayan da sojoji suka kwato shi a hannun su amma hakan ya faskara

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China