in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Jami'in kasar Sin ya bayyana niyyar kasar ta kyautata dangantakar dake tsakaninta da kasashen Larabawa
2016-01-14 11:19:18 cri
A yau ne jaridar People's Daily ta kasar Sin ta wallafa sharhin da ministan harkokin wajen kasar Sin Wang Yi ya gabatar mai taken "samar da kyakkyawar makoma kan raya dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Larabawa", inda ya yi bayani kan muhimmancin takardar manufofin da Sin ta gabatar game da kasashen Larabawa, kana ya yi kira da a yi amfani da shirin nan na "ziri daya da hanya daya" wajen raya dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Larabawa.

Sharhin ya bayyana cewa, shekarar bana shekara ce ta cika shekaru 60 da kulla dangantakar diplomasiyya a tsakanin Sin da kasashen Larabawa. Don haka, gwamnatin kasar Sin a karon farko ta gabatar da takardar manufofin game da kasashen Larabawa, wadda ke da muhimmanci matuka

Sharhin ya kuma yi kira da a yi amfani da shirin nan na "ziri daya da hanya daya" da shugaban kasar Sin Xi Jinping ya gabatar, da yin hadin gwiwa da raya dangantakar dake tsakanin Sin da kasashen Larabawa, ta yadda za a samar da sabbin damammaki ga hadin gwiwar da ake yi tsakanin sassan biyu. (Zainab)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China