in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
Yarjejeniya kan aikin gona ce da za ta kawar da shingen cinikayya, in ji kasashen Afirka
2015-12-18 09:44:21 cri

Kasashen nahiyar Afirka sun yi kiran da a bullo da wata yarjejeniya da za ta dace da muradun kasashe masu tasowa, a matsayin wata kafa ta kawar da shingen cinikayya da kasashen suka shafe kimanin shekaru 15 suna fuskanta

Babban sakatare a ma'aikatar harkokin kasashen waje ta kasar Kenya Karanja Kibicho ne ya bayyana hakan yayin taron ministocin kungiyar cinikayya ta duniya wato WTO a takaice da ke gudana yanzu a haka a kasar Kenya.

Ministocin kasashen da ke halartar wannan taro da suka hada da na Benin, Burkina Faso, Chadi da Mali, sun amince cewa, muddin ba a cimma yarjejeniyar da za ta kai ga kawar da rangwame kan amfanin gona a taron na birnin Nairobin Kenya ba, hakika za su nemi yin hakan a gaban kotu.

Ministan harkokin tattalin arziki na kasar Chadi Aziz Mahamat Saleh ya ce, idan har aka cimma wannan yarjejeniya ta kawar ta rangwame kan amfani gano, hakan zai taimaka wajen samar da daidaito a nahiyar Afirka, lamarin da zai kara taimakawa kasashen amfana da sassan cinikayya cikin 'yanci.

Mahalarta taron na Kenya sun amince cewa, dandalin na WTO, shi ne dandalin da ya dace ga kasashe na Afirka da ragowar masu ruwa da tsaki, wajen samun dabarun da suka bukata ta yin gogayya a harkokin cinikayya.(Ibrahim)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China