Babban kwamitin kasa na yaki da cutar kanjamau na kasar Congo ya rarraba, tare da hadin gwiwar asusun ci gaban jama'a na MDD UNFPA, hular mazakuta fiye da dubu 94 a wurare daban daban da aka kebe, har ma da gidajen otel otel da suka karbi tawagogin mahalarta gasannin Afrika na shekarar 2015.
Wani irin kamfe ne da ke gudana a ko ina cikin duniya, musammun ma a lokacin da ake gudanar da manyan bukukuwan wasanni domin baiwa matasa kwarin gwiwa da su kare kansu, da tabbatar da yanayin hidima, domin kada wannan yanayi ya koma wani tashin hankali na daukar juna biyu ba cikin ana so ba, ko kamuwa da cututtukan irin na jama'i, in ji kungiyar UNFPA. (Maman Ada)