in Web hausa.cri.cn
ShigaZaman RayuwaAfirka a YauSin Ciki da WajeAmsoshin TambayoyiWasannin Motsa JikiChina ABC::: TSOHO :::
An sake gano wadansu mutane 3 dauke da Ebola a Saliyo
2015-09-09 11:00:55 cri
Hukumar kula da agajin gaggawa na cutar Ebola na gwamnatin Saliyo ta tabbatar da cewa ta sake samun labarin cutar ya kama mutane 3 a ranar litinin din makon nan, bayan da kasar ta samu mutum daya da ya mutu sakamakon annobar a makon jiya.

Kakakin hukumar Yayah Tunis ya shaida ma kamfanin dillancin labarai na kasar Sin Xinhua cewa, duk mutane ukun da aka tabbatar sun kamu da cutar sun fito ne daga kauyen Sellakafter, kuma 'yan uwa ne na jiki ga wata tsohuwa 'yar shekaru 67 da ta rasu sakamakon cutar a kauyen.

Yanzu wannan adadin ya zama mutane hudu ke nan da aka tabbatar suna dauke da cutar a kasar baki daya, sannan dukkansu an riga an killace su don hana yaduwar cutar.

Yayah Tunis da yake karin haske a kan al'amarin ya ce, yanzu haka dangin marigayiyar na daga cikin mutane 50 dake fuskantar hadari matuka a kauyen, kuma hukumar tana lura da su kwarai, ya ce duk da dai su ma sun damu amma ya fi sauki a kebe su tun da an riga an killace gidan da suka fito ainihi.

Ya jaddada sakon hukumar ga al'umma da su kiyaye ka'idoji na tabbatar da ba su taba ko wanke jikin mamaci ba, kuma su kira cibiyar kula da aikin hana yaduwar cutar cikin gaggawa idan danginsu ya kamu da rashin lafiya.

Ya bayyana cewa, hukumar ta kara aikawa da karin jami'ai a yankunan da cutar ta bulla duk a cikin kokarin wayar da kan jama'a.(Fatimah Jibril)

Labarai masu Nasaba
Ra’ayoyinku
  Webradio
Saurare (GMT 11:30pm - 12:30pm)
Bayanai da Dumi-dumi
© China Radio International.CRI. All Rights Reserved.
16A Shijingshan Road, Beijing, China